Bayani game da mu

An samar da Tsangayar Africa ne da nufin taimaka wa al’umar Africa, wajen samun ingantacciyar fahimtar Musulunci, ta hanyar Ƙur’ani Mai Girma, da Sunnar Annabi ﷺ.

Dandali ne  shakundum wanda  ke gabatar da shirin ilimantarwa da nufin kusantar da  ilimi  zuwa ga masu sha’awar shi, ta hanyar Internet, da kafofin  sada zumunta, da kuma kan akwatin talabijin na Africa tv3. 

Dandalin ya dogara da samar da ilimi mai zurfi akan tsarin: Massive Open Online Course wanda ake taƙaita shi da kalmar (MOOCs) Tsangayar  tana aiki ne 100%
ta Internet    inda ɗalibai za su iya shiga darussa ta hanyar kwamfuta da na’urori masu  ƙwaƙwalwa, kuma suna  iya halartar  bitoci  ta hanyar darussan da aka ɗauke su ta hanyar bidiyo da kuma   littattafan amfanin na’ura mai ƙwaƙwalwa, da kuma  amsa tambayoyin auna fahimta.

Kuma ta dogara da fitattun malamai  masu wa’azi na  Ahlus Sunna  Wal Jama’a masu magana da harshen Hausa.

Buri

Muna burin mutum dubu goma su shiga wannan tsarin a zango ukun farko.

Saƙo

Tsangayar Africa ta zamanto jagora a fagen koyarwa da harshen Hausa ta hanyar Internet, da hanyoyi na zamani, da kuma kafafen da suke da dangantaka da Tsangayar Africa, da sauran shafukan Internet mabambanta.

Manufofi

  1. Biyan buƙatar musulmai game da ilimin shari’a daga tushe, da kuma sanar da ɗalibi abin da dole ne a ce duk ɗalibin ilimi ya san shi, da harasan Africa.
  2. Yaɗa Aƙidar  Ahlus Sunna Wal Jama’a, da ingantaccen ilimin Fiƙihu tare da dalilansa na Ƙur’ani da Sunna.
  3. Koyar da mata musulmai addininsu, da wayar da su, da kuma bayar da gudunmawa wajen horar da mata ɗaliban ilimin Shari’a.
  4. Yaɗa wayewar koyon ilimin Shari’a ta hanyar Internet a Africa, ta hanyar samar da manhajar ilimi, wadda take kula da ƙwarewa, da ƙirƙira a wajen salon bijiro da ilimi.

Buri

Muna burin mutum dubu goma su shiga wannan tsarin a zango ukun farko.

Misheni

Tsangayar Africa ta zamanto jagora a fagen koyarwa da harshen Hausa ta hanyar Internet, da hanyoyi na zamani, da kuma kafafen da suke da dangantaka da Tsangayar Africa, da sauran shafukan Internet mabambanta.

Malengo

  1. Biyan buƙatar musulmai game da ilimin shari’a daga tushe, da kuma sanar da ɗalibi abin da dole ne a ce duk ɗalibin ilimi ya san shi, da harasan Africa.
  2. Yaɗa Aƙidar  Ahlus Sunna Wal Jama’a, da ingantaccen ilimin Fiƙihu tare da dalilansa na Ƙur’ani da Sunna.
  3. Koyar da mata musulmai addininsu, da wayar da su, da kuma bayar da gudunmawa wajen horar da mata ɗaliban ilimin Shari’a.
  4. Yaɗa wayewar koyon ilimin Shari’a ta hanyar Internet a Africa, ta hanyar samar da manhajar ilimi, wadda take kula da ƙwarewa, da ƙirƙira a wajen salon bijiro da ilimi.